Friday, September 12, 2025
23.1 C
Abuja

An hallaka sama da mutane 70 a harin da aka kai birinin Mali

An hallaka sama da mutane 70 a harin da aka kai birinin Mali

Wata majiyar tsaro da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa mutane 77 ne suka mutu yayin da wasu 255 suka samu raunuka a hare-haren na ranar Talata a birnin Bamako.

Wani harin ‘yan tada kayar baya a babban birnin kasar Mali wanda aka yi nufin kai wa sansanin horar da ‘yan sandan soji da filin jirgin sama ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 70 tare da raunata wasu 200, daya daga cikin mafi muni da jami’an tsaro suka gani a shekarun baya.

Wata majiyar tsaro da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa mutane 77 ne suka mutu yayin da wasu 255 suka samu raunuka a hare-haren na ranar Talata a birnin Bamako.

Ingantacciyar takarda ta sirri ta ce adadin wadanda suka mutu ya kai 100, inda ta bayyana sunayen mutane 81 da abin ya shafa.

Jaridar Le Soir ta ranar Alhamis ta ruwaito cewa za a yi jana’izar daliban ‘yan sandan soji kusan 50 a ranar.

Na farko irinsa a cikin shekaru

Kawo yanzu dai hukumomin sojin Mali ba su fitar da takamaiman adadin wadanda suka mutu sakamakon harin ba, wanda kungiyar JNIM mai alaka da Al-Qaeda ta dauki alhakin kai harin.

Wannan hari dai shi ne irinsa na farko cikin shekaru da dama da suka gabata, kuma ya kada hantar cikin gwamnatin mulkin soja, kamar yadda masana suka ce.

Babban birnin kasar Mali dai ya tsallake rijiya da baya daga hare-haren da ake kai wa akai-akai a wasu sassan kasar da ke Yammacin Afirka.

Babban hafsan sojin ya yarda da yammacin ranar Talata cewa “an yi asarar wasu rayukan mutane”, musamman ma’aikata a cibiyar ‘yan sanda ta sojoji.

Juya wa ECOWAS baya

JNIM ta yi iƙirarin cewa wasu ƙalilan daga cikin mayakanta sun kashe tare da raunata “daruruwa” daga bangaren hamayya, ciki har da mambobin ƙungiyar sa-kai na Rasha Wagner.

Harin dai ya zo ne kwana guda bayan da kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso karkashin jagorancin mulkin soja suka cika shekara guda da kafa kungiyarsu ta kawancen kasashen Sahel (AES).

Ƙasashen uku, wadanda ke karkashin mulkin soji tun bayan juyin mulkin da aka yi ta yi tun shekara ta 2020, sun karya alaka da tsohuwar ‘yar mulkin mallaka ta Faransa inda suka karkata a fagen soji da siyasa zuwa sauran abokan hulda da suka hada da Rasha.

Hot this week

“Shehu Sani Warns: Ukraine to Lose Land to Russia, $500bn Minerals to US Amid War Fallout”

The ongoing war between Ukraine and Russia continues to...

Pope Francis’ Health: Doctor Says Pontiff ‘Not Out of Danger’ Amid Recovery

Pope Francis’ personal physician, Dr. Sergio Alfieri, has given...

Trump Sparks Controversy Over 14th Amendment, Claims Birthright Citizenship Was Never Meant for Immigrants

Trump Challenges Birthright Citizenship in New Executive Order President Donald...

Trump announces he will implement tariffs on products from the EU

U.S. President Donald Trump has once again emphasized his...

“America, China And The World As Trump Returns”

When Huge Fortune Is Involved There Is No Price...

Topics

Eniola Badmus Reaffirms Her Support for President Tinubu, Sparking Reactions

Eniola Badmus, a well-known actress and Special Assistant for...

Rapper Jeriq Explains Why He Has Never Been in a Relationship

Nigerian rapper Jeremiah Chukwuebuka Ani, widely known as Jeriq,...

Album Releases: Ruger and Joeboy Face Off in a Supremacy Battle

The Nigerian music scene is buzzing with excitement and...

“Famous singer NBA YoungBoy has been released from prison.”

Popular American singer Kentrell DeSean Gaulden, better known as...

“My kind of wealth cannot be achieved through investment,” Davido proudly declared.

Nigerian Afrobeats singer David Adeleke, widely known as Davido,...

“I backed Tinubu, but the hardship is becoming unbearable,” said Cynthia Morgan.

Nigerian singer Cynthia Morgan, now known as Madrina, has...
spot_img

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img