Friday, September 12, 2025
26.1 C
Abuja

Mutanen da suka mutu sun fi 300 a sudan saboda annoban kwalara

Mutanen da suka mutu sun fi 300 a sudan saboda annoban kwalara

Ɓarkewar annobar ta shafi jihohi tara, inda aka ba da rahoton mutane 11,000 sun kamu.

Adadin wadanda suka mutu sakamakon barkewar cutar amai da gudawa a Sudan ya kai 348 a cewar ma’aikatar lafiya.

Barkewar cutar ta shafi jihohi tara, inda sama da mutane 11,000 suka kamu da cutar. Bugu da ƙari, ana nuna damuwa game da yiwuwar ɓarkewar zazzabin dengue, bayan mutuwar wasu mutane biyu da ake zargin sun kamu da cutar.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ambaliya sun ta’azzara yaduwar cutar kwalara tun watan Yuni.

Tsarin kiwon lafiya mara inganci a Sudan da yaƙi ya ɗaiɗaita, ya ƙara dagula ƙoƙarin da ake yi na daƙile cututtuka masu yaɗuwa.

Annoba

A watan Agusta Ministan lafiya na Sudan ya ayyana bullar cutar kwalara bayan shafe makwanni ana ruwan sama kamar da bakin kwarya a kasar da yaki ya daidaita, kamar yadda aka nuna a wani faifan bidiyo da ma’aikatarsa ​​ta fitar.

Haitham Ibrahim ya ce an dauki matakin ne tare da hadin gwiwa da hukumomi a jihar Kassala da ke gabashin kasar, da hukumomin Majalisar Dinkin Duniya, da kwararru bayan “dakin binciken na lafiyar jama’a ya gano kwayar cutar ta kwalara.”

Tun a watan Afrilun 2023 ne dai kasar da ke arewa maso gabashin Afirka ke fama da yaki tsakanin sojojin Sudan karkashin shugaban kasar Abdel Fattah al-Burhan da kuma dakarun Rapid Support Forces (RSF), karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdan Daglo.

Rikicin ya haifar da daya daga cikin mafi munin rikicin jin kai a duniya, inda sama da mutane miliyan 25 – sama da rabin al’ummar kasar – ke fuskantar matsananciyar yunwa.

Karancin abinci

An ayyana yanayin yunwa a wani sansanin gudun hijira a babban yankin yammacin Darfur.

Dubban mutane ne suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa, lamarin da ya haifar da karuwar cututtuka da suka hada da gudawa, musamman ga yara.

Kwalara na haifar da zawo mai tsanani da amai da ciwon jiki, kuma galibi tana faruwa ne ta hanyar ci ko shan abinci ko ruwan da ya gurbata da kwayoyin cutar, a cewar hukumar lafiya ta duniya.

Tana iya haifar da rashin ruwa a jiki mai tsanani, wanda zai iya kai wa ga mutuwa a wasu lokuta a cikin ‘yan sa’o’i.

Hot this week

“Shehu Sani Warns: Ukraine to Lose Land to Russia, $500bn Minerals to US Amid War Fallout”

The ongoing war between Ukraine and Russia continues to...

Pope Francis’ Health: Doctor Says Pontiff ‘Not Out of Danger’ Amid Recovery

Pope Francis’ personal physician, Dr. Sergio Alfieri, has given...

Trump Sparks Controversy Over 14th Amendment, Claims Birthright Citizenship Was Never Meant for Immigrants

Trump Challenges Birthright Citizenship in New Executive Order President Donald...

Trump announces he will implement tariffs on products from the EU

U.S. President Donald Trump has once again emphasized his...

“America, China And The World As Trump Returns”

When Huge Fortune Is Involved There Is No Price...

Topics

Eniola Badmus Reaffirms Her Support for President Tinubu, Sparking Reactions

Eniola Badmus, a well-known actress and Special Assistant for...

Rapper Jeriq Explains Why He Has Never Been in a Relationship

Nigerian rapper Jeremiah Chukwuebuka Ani, widely known as Jeriq,...

Album Releases: Ruger and Joeboy Face Off in a Supremacy Battle

The Nigerian music scene is buzzing with excitement and...

“Famous singer NBA YoungBoy has been released from prison.”

Popular American singer Kentrell DeSean Gaulden, better known as...

“My kind of wealth cannot be achieved through investment,” Davido proudly declared.

Nigerian Afrobeats singer David Adeleke, widely known as Davido,...

“I backed Tinubu, but the hardship is becoming unbearable,” said Cynthia Morgan.

Nigerian singer Cynthia Morgan, now known as Madrina, has...
spot_img

Related Articles

Popular Categories

spot_imgspot_img